05/04/2026
Da Addini Ake Shirya Jana’izarmu!
Akwai wani mataki da in jahilcinka ya kai to hakan yana zama babban makami ne a hannun makiyanka.
Abin da yake faruwa a Najeriya a halin yanzu, musamman abubuwan da s**a shafi rikicin Jos da sauran sassan kasar nan, ba yaki ne na neman gaskiya ko bayyana ta ba; Surgical Operation ne da aka kera don raba zuciyar talaka musulmi da talaka kirista.
Kafin bayyanar wadannan mutane biyu da kuke gani, musamman wannan bako mai suna Alex, al’ummar kasar nan suna da wani tsari na Tolerance (hakuri da juna). Sun san cewa duk wanda zai biyo dare ya kashe mutane, bazai tambayeka addini ba kafin ya harba harsashi.
Amma yau, an shigo da gubar da take nuna wa kowane bangare cewa shi kadai ake nema a kashe, musamman kiristoci sunfi Shan wannan gubar duk da sanin gubar zatayi musu illa anan gaba.
Wannan bawan Allah mai suna Alex yana tafiya ne da ajandar da muke kira Divide and Rule (Raba ka mulka). Yana rura wutar cewa wai kiristoci ne kawai ake hara, alhalin gaskiyar magana ita ce, harsashin bindiga baya zabar fata ko aqida; musulmi ma kashe su ake yi, kiristoci ma ana kashe su.
Abin bakin ciki shi ne, idan wannan wutar ta Religious War tafi karfin kiristocin, Alex fa ba zai tsaya ya gani ba, Kuma bazai tsaya ya karesu ba. Yana da Dual Citizenship, yana da International Passport. Da zarar jini ya fara malala a titunan Jos ko Kaduna, zai dauki kayansa ya koma kasashen waje ya bar ni da kai muna karar da kanmu, k**ar yadda na samu Labarin harya gudu ya barmu.
Yakin addini ba k**ar harin ‘yan ta’adda ba ne; ‘yan ta’adda suna bugawa ne su gudu, amma yakin addini ciwo ne da yake zama a gida, yana tashi da safe, ya kwanta daddare, kuma babu gwamnatin da ta isa ta tsayar da shi muddin zuciya ta riga ta baci.
Ya k**ata mu tambayi kanmu: Wane ne yake cin ribar wannan?
Ilimin Physics ya koya mana cewa duk inda aka samu Friction (gogayya), to ana samun Heat (zafi). Wannan zafin da suke samarwa a tsakaninmu shi ne yake ba su damar cigaba da satar😡