13/06/2026
CDCFIB TA SANAR DA MATAKI NA GABA A DAUKAR MA’AIKATA NA 2024/2025.
Hukumar kula da daukar ma’aikata ta hukumar tsaron gidajen gyaran hali, kashe gobara da shige da fice (CDCFIB) tana sanar da al’umma baki daya, musamman wadanda s**a nemi aikin daukar ma’aikata na shekarar 2024/2025, cewa za'a fara mataki na gaba na aikin, wato tantance lafiyar jiki da kuma tabbatar da takardu.
Saboda haka, duk masu neman aikin da s**a rubuta jarabawar kwamfuta (CBT) da aka gudanar a watan Nuwamba 2025, su shiga shafin daukar ma’aikata na hukumar daga Litinin 15 ga Yuni zuwa Juma’a 20 ga Yuni, 2026, domin duba matsayin aikace-aikacensu.
Ana bukatar masu neman aikin su shiga da (Application Number) da aka ba su lokacin yin rajista.
Idan an zabe su, za'a bukace su da su loda takardunsu, sannan su zabi rana da wurin da s**a fi so domin halartar tantancewar jiki.
Ana shawartar masu neman aikin da su bi duk umarnin da aka bayar a shafin.
Hukumar tana jaddada cewa duk tsarin daukar ma’aikatan kyauta ne gaba daya.
Saboda haka, kada wani ya biya kudi ga kowane mutum, wakili, kungiya ko wata hukuma da ke ikirarin za ta taimaka wajen saka sunansa cikin jerin wadanda aka zaba, ware masa wurin tantancewa, loda takardu, samun damar shiga wurin tantancewa ko samun zabe na ƙarshe.
Haka kuma, ana gargadin jama’a da su yi watsi da sakonnin bogi, hanyoyin yanar gizo na damfara, da kuma mutanen da ba su da izini da ke ikirarin wakiltar hukumar.
Duk wasu sahihan bayanai za'a fitar da su ne ta hanyar shafin daukar ma’aikata na CDCFIB da sauran hanyoyin sadarwa na hukuma da aka amince da su.
Hukumar na ci gaba da tabbatar da cewa an gudanar da aikin daukar ma’aikatan cikin gaskiya, adalci, cancanta da kuma bin dokoki da ka’idojin da s**a tanada.
Link yana comment section.
Allah ya bada nasara.