05/11/2023
Matashin Dan jaridarnan Mai suna Comr Abba Sani Pantami
Yabawa "yan Nigeria shawara ta musamman Akan hadin kai
Wannan shine rubutun da yawallafa Ashafinsa na Facebook👇
Manyan 'yan kasuwar mu na Arewa da ya kamata su hada kansu don cigaba da bunkasa harkokin su da taimakon yankin, da daga darajar yankin a idon Duniya, yanzu suna ta fada a tsakanin su.
Talakawan Arewa da ya kamata su hada kansu don taimakon juna, amma kyashi, hassada da son zuciya yasa sun kasa hada kai.
Matasan Arewa da ya kamata sufi kowa kishi da hadakai, don gina rayuwarsu da taimakon junansu, amma hassada da bakin ciki ta dabai-baye zuciyoyinsu sun koma yakar junansu da kansu.
Iyaye, Sarakuna da ya kamata su jagoranci al'ummar Arewa don ganin an samu hadin kai da cigaba, amma sunyi shiru abunsu kowa ta kanshi da sarautar shi yake.
Shugabanni da 'yan siyasar Arewa da dama daga cikin su, bama Arewa bace a gaban su ba, mulkin su da iyalansu sune a gaban su.
Malamai, jagororinmu da ya kamata su tinashemu abunda ya dace, tuni an farraqa tsakanin su, an haddasa rikice-rikice masu yawa a tsakanin su, har yau sun kasa yin tasiri don taimakon yankin.
Shin wai sai yaushe al-ummar Arewa zasu hada kai, don taimakon junansu?
Shawara a gareka matashi dan uwana, ka daina tunanin cewa manyan Arewa zasu taimakeka, ka tsaya kayi karatun ta nutsu ,ka samawa kanka mafita da zaka taimaki kanka da mutanen da ke tare dakai, kada ka yadda hassada, kyashi, bakin ciki ya hadaka da uwanka.
✍️ Comr Abba Sani Pantami