Kiran Sayyed Zakzaky

Kiran Sayyed Zakzaky ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMAD WA,ALIY MUHAMMAD

Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) Ya kawo cewa:“Allah Ta'ala yana cewa:يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِنْ تَنْصُرُوا ا...
19/05/2026

Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) Ya kawo cewa:

“Allah Ta'ala yana cewa:

يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِنْ تَنْصُرُوا اللَّهَ يَنْصُرْكُمْ وَيُثَبِّتْ أَقْدَامَكُمْ.

“Ya ku Muminai, idan kuka taimaki addinin Allah, Allah zai taimake ku, kuma ya tabbatar da dugaduginku.”

“Wannan alƙawari ne na Allah. Saboda haka, mu a nan har yanzu (azzalumai) suna tunanin kawai za su muttsike mu ne. Saboda haka, muna marhalan dauriya ne. Amma sun san cewa, marhala-marhala ne, akwai marhalan da yana nan tafe!

“La-muhalata yana tafe. Wannan ne lokacin da kuma tursasa mana din ba fa zai yiwu ba, mun fi ƙarfin wannan kuma.

“Hawa-hawa ne. Su ma s**an fada, s**an ce ya k**ata su gama da abin ne (Da'awa) tun bai yi karfi ba. Su ba su suna kuka suna yin ne yana ƙara ƙarfi ba. Da ma za su kyale ma, da sai ya daina ƙarfin. Amma ba za su ƙyale ba fa....

“Saboda haka, ina gaya mana ne, dole ne marhalan dauriya na nan, in babu wannan jarabawa, to tamkar ba Tabligin ake yi ba, domin Sunnar hanyar kenan. Ba canji ga wannan Sunnar kuma. Ita kenan, haka al'amarin ya gada. Haka aka yi ma na farko, haka za a yi ma na karshe, amma dai alƙawarin nasara Alhamdulillahi, Allah Ta'ala Ya yi mana.”

— A jawabinsa ga Muballigun, a yayin rufe Mu'utamar ɗin Lijanut Tarbiya wat-Tableeg, a ranar 15 ga Zulƙa'ada 1447 (3/5/2026) a gidansa da ke Abuja.

RANA TA FARKO: An Fara Gabatar Da Gagarumin Mu'utamar Ɗin Ƙasa Da Ƙasa A Jihar BauchiA yau Alhamis 16/04/2026 wanda ya y...
16/04/2026

RANA TA FARKO: An Fara Gabatar Da Gagarumin Mu'utamar Ɗin Ƙasa Da Ƙasa A Jihar Bauchi

A yau Alhamis 16/04/2026 wanda ya yi daidai da (28-10-1447H) ƴan’uwa musulmi Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky [H], sun fara gabatar da taron Mu'utamar ɗin ƙasa da ƙasa a jihar Bauchi, wanda taron shi ne karo na biyar da Harkar musulunci ƙarƙashin jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky [H] ke gabatarwa tun bayan waƙi'ar Buhari, domin kwakkwafa tunanin ƴan’uwa ƴan gwagwarmaya akan Fikira ingantacciya.

Shaikh Rabi'u Funtua, shi ne ya albarkaci taron da buɗewa da addu'a, sai mawaƙa su haskaka muhallin da waƙoƙi na shajja'a al'umma kan taimakon raunana da yaƙi da zalunci, da tsayawa ƙyam a kan tafarkin gaskiya.

Daga nan Sista Zahra'u Abubakar Katsina, ta karanto wasu ayoyi daga Alkur'ani mai girma cikin suratul Hujrat. Ɗan uwa Sidi Jawad ne ya gabatar da jawabin barka da zuwa.

Malama Maryam Sani ta gabatar da jawabin maƙasudin taro wanda ta bayyana cewa: "Idan kaje makaranta ka san cewa akwai abubuwan da za ka amfana da su, saboda haka akwai biro da takardar ka, da ka ji wani abu da baka sani ba, za ka rubuta. Wannan abin da ka tsinta, za ka yi amfani da shi, kuma sannan ka amfanar da wasu. Mun san cewa da yawan mutane suna son zuwa amma ba su samu zuwa ba. Wasu akwai dalilin rashin lafiya, wasu wani abu daban, wasu rashin kuɗin mota", in ji ta.

Ta ƙara da cewa: "Yana da kyau duk abin da muka ji, mu kai ma ƴan’uwan waɗanda ba su samu damar halarta ba, za mu samu ladan ji, zamu samu ladan isar da saƙo zuwa ga ƴan’uwan mu. Sannan yana da kyau duk abin da za mu yi a nan, ya kasance koyarwa ce ta addini, k**ar yadda muka sani mu masu da'awa ne, masu isar da saƙo ne. Duk abin da za mu yi, halayar mu wanda zamu nuna a nan, ya zama addini ne. Mu yi mu'amala k**ar yadda Allah ya ce mu yi."

Ta ƙara da jan hankalin Sistoci a kan kula da hijabi. Inda ta ce; "Mu kula da hijabanmu, mu yi ƙoƙari mu kiyaye shi", ta jaddada.

Bayan kammala jawabinta, wakilin ƴan uwa na Bauchi Shaikh Ahmad Yusuf Yashi, ya gabatar da jawabin maraba da baƙi. Daga ƙarshe aka yi addu'a aka sallami kowa zuwa masauki.

—Dandalin Yaɗa Labarai Na Taron


Rikicin Siyasar Samun Yanci Kai A Kano 1953 Wanda Akafi Sani Da Turanci (Kano Riot)Abin da ya jawo wannan tarzoma shi ne...
05/04/2026

Rikicin Siyasar Samun Yanci Kai A Kano 1953 Wanda Akafi Sani Da Turanci (Kano Riot)

Abin da ya jawo wannan tarzoma shi ne tabarbarewar dangantakar da ke tsakanin shugabannin siyasar Arewa da na Kudu a kan batun cin gashin kai a shekarar 1956. Wannan ya taso ne tun a shekarar 1953 da aka gabatar wa Majalisar Wakilai ta 1953.

Memba na Jama'iyar Action Group (AG), Cif Anthony Enahoro ya gabatar da kudiri a shekarar 1953 cewa: lokaci yayi da Najeriya zata samu ‘yancin kai a shekarar 1956. Shugabannin Arewa sun yi watsi da wannan kudiri. Lamarin ya ci tura wanda hakan ya haifar da rashin jituwa tsakanin shugabannin siyasar Arewa da na Kudu.

Kayar da kudirin ya harzuka jama’ar Legas, inda s**a mayar da martani Mai Zafi ga shugabannin siyasar Arewa inda s**a yi ta yi musu ihu da zagi a Legas, bayan dage zaman Majalisar a ranar 31 ga Maris, 1953.

Jam’iyyar (AG PARTY) ta ’yan kabilar Yarabawa ce zalla, (NCNC) ita kuma ta kabilar Igbo ce, kuma dukkansu sun amince da ’yancin kai a 1956, alhali kuwa ita Jam'iyar (NPC), wanda itace Jam'iyar Arewa tace bata amince ba. Sardauna jagoran Jam'iyar Yace: Arewa ba ta shirya a ba da mulki ba, dalilinsa shi ne, yan Arewa da yawa basu kammala karatun jami'a ba, su kuwa yan kudu tuni sunyi nisa a karatun boko, ba k**ar yan Arewa ba. Sardauna da sauran mayan Arewa sunji tsoron idan an bayar da mulki a 1956 yan kudu za su mamaye dukkan manyan muk**ai a Najeriya.

Wannan yasa Yan kudu su kai ta zagin Sardauna suna cewa ya hada baki da turawan mulkin mallaka don ka da a bai wa Najeriya yanci.

Da lokaci ya kure, AG da NCNC sun tura wasu mutane kano domin yin kamfen din goyon bayan neman yanci, hakan ya haifar da tashin hankali a Arewa lokacin da kungiyar Action Group ta ziyarci Kano a karshen mako na 15-17 ga Mayu, lamarin ya faru ne sak**akon kiyayyar da aka nunawa yan Arewa a Legas.

Da farko dai an gudanar da zanga-zangar cikin lumana wanda magoya bayan jam’iyyar Peoples Congress ta Arewa s**a gudanar

Amma washegari zanga-zangar ta rikide ta koma tarzoma.

Tashin hankalin ya fara ne a Otal din Turawan mulkin mallaka, a ranar 16 ga Mayu 1953 wanda a wurin za ayi taron jam'iyar Action Group karkashin jagorancin Akintola.

Kafin taron dai kungiyar ‘yan asalin Kano ta janye goyan bayanta da izinin da ta bayar nayin wannan taro. Daga bisani wasu gungun jama’a ne s**a taru a wajen otal din, inda s**a fara jifan mutanen da ke kusa da otal din, yayin da s**a tafka asara mai dinbin Yawa. Wasu mutane biyu da ake kyautata zaton ’yan Kudu ne sun mutu, daga bisani ’yan tarzomar sun yi yunkurin shiga Sabon Gari, amma jami’an ‘yan sandan kasar s**a fatattake su.

Lamarin ya kara ta’azzara kuma ya zama rikicin kabilanci a ranar 17 ga watan Mayu, lokacin da zauna Gari banza s**a fito daga yankin Arewacin Kano, musamman unguwar Fagge, wasu daga cikin masu tayar da tarzoma na dauke da bindigogi, s**a yi yunkurin kutsawa yankin Kudu da Ibo s**a mamaye yankin Sabon Gari, su kai sa'ar shiga, duk da cewa lamarin nasu na asali na kin Yarabawa ne, amma wadanda aka kashe a yankin Sabon Gari yawancinsu 'yan kabilar Igbo ne. Shaguna da suke ciki duk an wawashe su a Kasuwar Sabon Gari tare da kai munanan hare-hare.

An kira jami’an ‘yan sanda da na Sojoji tare da hana wasu barayin shiga yankin Sabon Garin. Rikicin ya ci gaba da barkewa a yankunan Kano musamman ma Fagge.

Bayan dokar hana fita a ranar 16 ga Mayu fadan ya lafa amma ya sake barkewa a washegari. A ranar 18 ga wata, an kai wani gagarumin dauki na 'yan sanda da sojoji zuwa Kano, an kuma kafa dokar ta-baci a duk fadin yankin. kuma an raba bangarorin da ke gaba da juna ta hanyar sa shingen waya.

Bayan Kura ta Lafa, an yi musayar fursunoni don a rage zaman dar-dar, an sako ’yan Kudu da aka k**a, su ma ’yan Arewa sun saki yan kudu, an bukaci ‘yan Arewa mazauna yankin Sabon Gari da su tashi, sannan aka bukaci ‘yan Kudu mazauna yankin Fagge da su koma Sabon Gari.

Kimanin ‘yan Najeriya 46 galibi ‘yan Arewa da kuma ‘yan kabilar Igbo ne s**a mutu a wannan arangamar, kuma an yi jinyar fiye da mutane 200 da s**a samu raunuka. Duk da cewa nan take gwamnatin mulkin mallaka a Najeriya ta kira abinda ya faru da rikicin kabilanci, amma shugabannin siyasa sun ce rikicin siyasa ne tsakanin mutanen da ke son mulkin kai a shekarar 1956 da kuma masu son ci gaba da mulkin mallaka.

13/12/2025
12/12/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Tasi'u Baban Sajjad, Abubakar Hassan

GAYYATA! GAYYATA! GAYYATA!Yan'uwa Musulmi Almajiyar Sayyid Zakzaky (H) da Da'irar Darazo na farin ciki n Sanar daku tare...
08/11/2025

GAYYATA! GAYYATA! GAYYATA!

Yan'uwa Musulmi Almajiyar Sayyid Zakzaky (H) da Da'irar Darazo na farin ciki n Sanar daku tare da gayyatar ɗaukakin al'umma zuwa gagarumin katamar Mauludin fiyayyen Halitta Annabi Muhammad (saw). wanda za ayi k**ar haka:

Ranar Lahadi 09/11/2025 18/06/1447
Lokaci: 08:00pm
wuri: Ƙofar Babban Masallacin Fada, Darasi

Babban Baƙo mai jawabi
Sheikh Sa'idu Ibrahim Birnin kudu.

Allah ya bada ikon halarta.

ZIKIRAR TUNAWA DA WAƘI'AR BUHARIHarisawan Harkar musulunci ƙarƙashin jagorancin Sayyid Zakzaky (H) na Darazo Unit, Amiru...
24/08/2025

ZIKIRAR TUNAWA DA WAƘI'AR BUHARI

Harisawan Harkar musulunci ƙarƙashin jagorancin Sayyid Zakzaky (H) na Darazo Unit, Amirul Muminina Zone sun shirya kuma zasu gabatar da Zikira don tunawa da Shahidan Harkar musulunci na waƙi'ar Buhari.

Shahidan sunyi Shahada ne a garin Zaria shekaru Goma da s**a gabata bisa Jagorancin tsohon Shugaban Sojojin Nigeria Gen. Yusuf Tukur Burtai bisa umurnin tsohon shugaban Nigeria kuma Marigayi Gen. Buhari (LA).

Za a gabatar da zikirar ne k**ar haka:

Rana: Litinin 01-03-1447
25-08-2025
Lokaci: 04:00pm
Muhalli: Fudiyyah Darazo.

_Hurras Harkatul Islamiyya, Darazo Unit.



30/Safar/1447
24/August/2025

*KATAMAR ZAMAN MAKOKIN ASHURA A DA'IRAR DARAZO*Yan'uwa musulmi Almajiran Sayyid Zakzaky (H) da Da'irar Darazo dake jihar...
06/07/2025

*KATAMAR ZAMAN MAKOKIN ASHURA A DA'IRAR DARAZO*

Yan'uwa musulmi Almajiran Sayyid Zakzaky (H) da Da'irar Darazo dake jihar Bauchi sun gabatar da katamar zaman juyayin Shahadar Imam Hussain (As) ɗan Fatima yar Manzon Allah (SAW) wanda aka shahadantar dashi a filin Karbala a shekara ta sittin da ɗaya (61) bayan Hijira Manzon Allah daga Makka zuwa Madina.

An fara zama makokin ne tun daga ranar ɗaya ga wannan wata na Almuharram zuwa goma ga watan.

An kammala zaman a jarabawar Babban Masallacin Juma'a na Garin Darazo.

Malam Abdullahi Musa ɗaya daga cikin Malamai kuma Almajiran Sayyid Zakzaky (H) na garin Darazo shine ya gabatar da jawabi. A yayin jawabin nasa Malam ya karanto kissosi tare da darusan dake cikin waƙi'ar ta Ashura.

A karshe wakilin yan'uwa na Da'irar Darazo da kewaye Mal. Muhammad Inuwa ya rufe da Addu'a.

Forum Darazo
__06/07/2025
__10/01/1447

*AN GABATAR DA LUNCHING ƊIN LITTAFI RAYUWATA NA JAGORA SHEIKH IBRAHIM YAQUB AL-ZAKZAKY (H) A DA'IRAR DARAZO DA KEWAYE*A ...
01/05/2025

*AN GABATAR DA LUNCHING ƊIN LITTAFI RAYUWATA NA JAGORA SHEIKH IBRAHIM YAQUB AL-ZAKZAKY (H) A DA'IRAR DARAZO DA KEWAYE*

A daren ranar juma'a 01/05/2025 dede da 03/10/1446 yan'uwa Musulmi Almajiran Sayyid Ibrahim Al-Zakzaky (H) na Da'irar Darazo da kewaye s**a gabatar da lunchin ɗin littafin "RAYUWATA" wadda Sayyid Zakzaky (H) ya rubuta da kansa tare da kaddamar da shi Abuja.

Taron lunchin ɗin littafin "RAYUWATA" dake kunshe da tarihin jagoran harkar Musulunci a Nijeriya, watau Sayyid Zakzaky (H) ya samu halartar Waƙilai daga Central Working Commeety na Abuja a ranar Alhamis 03/05/2025.

A yayin gabatar da taro, bayan buɗewa da Addu'a, Malam Muhammad Auwal Darazo ya gabatar takaitaccen jawabi akan hadafin yin wannan lunching din inda daga bisani ya gabatar da wakilin central working committee daga Abuja, ya yayin jawabin sa wakilin ya gabatar da tsokaci dangane da littafin tarihin rayuwar shaikh Zakzaky (H) tare bayanin abin da littafin ya kunsa a takaice, k**a daga rayuwar su Malam (H) a makaranta, karatukansa , yanda ya fara da'awarsa, zamansa a kurkuku da sauran su.

Waƙilan ya ja hankulan yan'uwa kan Cewa, su yi ƙoƙari wajen ganin sun mallaki lattafin nan da ke ɗauke da tarin darussa daga rayuwar sayyid Zakzaky (H) a ɗeɗe ku ko a lajanoni.

A karshe, Da'irar Darazo da sunyi lonching na Littafin "RAYUWATA" akan kuɗi Naira Miliyan ɗaya da dubu ɗari baƙwai da talatin da biyar (₦1,735000). Daga bisani dai-dai kun yan'uwa nasu lunching ɗin akan mataki daban-daban.

Malam Saifullahi Ningi shine ya gabatar da Addu'ar rufewa, aka sallami yan uwa, s**a koma zuwa ga muhallansu.

Allah ya kara wa Jagora Sayyid Zakzaky (H) lafiya da nisan kwana, ya kuma bamu ikon Mallakar Wannan littafi baki ɗayan mu.

Forum Darazo






01–May–2025
03-Zhulqa'ada-1446

*ACI GABA DA GABATAR DA ZIYARORIN SA*Malam Mujahid Danjuma ɗalibi daga *KULLIYATUL MA'ARIF TABI'A LIL AT_BATUL HUSAINIYY...
23/03/2025

*ACI GABA DA GABATAR DA ZIYARORIN SA*

Malam Mujahid Danjuma ɗalibi daga *KULLIYATUL MA'ARIF TABI'A LIL AT_BATUL HUSAINIYYA AL_MUQADDASA DAKE ƘASAR IRAQ* ya ziyarci yan'uwa Musulmi Almajiran Sheikh Zakzaky (H) dake a garin Gabciyari karamar hukumar Darazo ta jihar Bauchi.

Ya ziyarci yan'uwan ne a ranar Juma'ar data gabata 22 ga Ramadan, 1446 dede da 22 ga march, 2025 a garin na Gabciyari.

Ya yayi ziyarar tasa sun tattauna abubuwa muhimma da s**a shafi Addinin Musulunci dama muhimman ayyukan da s**a hau kan dun wani Musulmi a wannan wata mai rahama na Ramadan.

Musab Darazo

23 Ramadan, 1446
23 March, 2025


Address

Zaria

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00

Telephone

08039297422

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kiran Sayyed Zakzaky posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share