18/04/2026
CIN ZARAFIN ADDINI DA TAUYE HAKKI NA DOKAR QASA!
Yanzu naga Labarin
Wata Daliba Musulma tazo zata shiga gurin da zasu rubuta jarabawa ta JAMB sai wata jami'ar tsaro na Civil Defence ta hanata shiga, ta koreta saboda hijabin ta
Amma ga wasu Dalibai sun zo tsirara an barsu sun shiga ba tare da wata tsangwama ba😢
Wannan cin zarafi da tauye hakkin addini da wulakanci ya faru ne a makarantar Peter Harvard School dake Kubwa a garin Abuja
Dokar Kasar Nigeria ya bawa kowa damar yin addininsa yadda ya ga dama ba tare da cutarwa, saka hijabi a gurin mace Musulma addini ne ba wai ganin dama ba
Abinda wannan jami'ar tsaro tayi fito na fito da dokar Kasa ne, wanda ya kamata a gudanar da kwakkwaran bincike domin ta fuskanci hukunci, domin zai iya haddasa fitina da tashin h@nkali
Kuma wannan yana kara bayyana mana cewa Musulmin Nigeria an gama cinye mu da yaki, ku yi tunanin in ba Musulma bace tazo zata shiga sai akace dole sai ta saka Hijabi? me kuke tunanin zai faru?
Yawan mu ya zama kamar bai da wani amfani, irin wannan wulakanci da cin fuska ya kamata ace ya jima da zama tsohon yayi🗣
Allah Yasa Mudace 🙌